'Yan Najeriya ku kara hakuri, nan ba da jimawa ba komai zai daidaita- CBN
Gwamnan Babban Bankin Najeriya "CBN" Dr. Oluyemi Cardoso ya roki 'yan kasar da su kara hakuri, bankin na iya bakin kokarinsa na ganin cewa ya dawo da darajar kudin kasar, wanda shi ne ya haifar da tsadar rayuwa da kasar ke mafa da shi.
Wallafawa ranar:
Mista Cardoso ya bayyana hakan ne yayin wani taro da ya gudana a Jami'ar Tarayya ta Ibadan, wanda ya samu wakilcin daya daga cikin jami'an bankin Dr. Usman Opanachi.
Jaridar Vunguard da ake wallafa a kasar ta ruwaito cewa, gwamnan Babban Bankin ya bayyana cewa, duk lokacin da darajar Naira ta shiga wani hali, bankin shima ya na shiga mawuyacin yanayi, saboda haka, ana aiki tukuru akai domin ganin cewa komai ya daidaita.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu