Isa ga babban shafi
GASAR AFCON

Najeriya, DR Congo, Afrika ta Kudu da Cote D’Ivoire sun kai matakin kusa da karshe

A gasar cin kofin Afrika,kungiyar Cote D’Ivoire mai masaukin baki ta lallasa kasar Mali da ci  2 da 1, yayinda Afrika ta Kudu ta doke Cap Vert ,nasarar da ke baiwa kungiyar damar tsallakawa matakin daf da na karshe a wannan gasa.

Kofin Kwallon kafar Africa
Kofin Kwallon kafar Africa © Goal
Talla

Yanzu kam kungiyoyi hudu ne suka rage a wannan tafiya,kuma daya daga cikin wadanan kungiyoyi da suka hada da Najeriya,Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo,Afrika ta Kudu da Cote D’Ivoire mai masaukin baki ne za ta dage wannan kofi.

'Yan wasan Najeriya a gasar AFCON
'Yan wasan Najeriya a gasar AFCON AP - Sunday Alamba

A bangaren Najeriya,wannan kungiya ta taba haduwa da Afrika ta kudu lokacin yan wasa irin su Jay Jay Okocha a shekara ta 2000 a wannan mataki na wasan daf da na karshe,wanda Najeriya ta yi nasara da ci 2 da nema kafin daga bisani Kamaru ta doke ta a wasan karshe.

Kofin gasar AFCON
Kofin gasar AFCON SuperSport

Haka zalika Cote D’Ivoire ta taba haduwa da wannan kungiya a 2015 a wannan mataki karkashin jagorancin mai horarwa Herve Renard,inda Cote D’Ivoire ta lallasa DRCongo da ci 3 da 1.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.