Sojojin Mali sun gano makeken kabari a Kidal bayan koran 'yan ta'adda
Sojojin Mali sun sanar da gano wani makeken kabari a Kidal da suka kwato kwanan nan daga hannun 'yan tawayen Abzinawa.
Wallafawa ranar:
Talla
Rundunar ta bayyana cewa, gano wannan kabari ya tabbatar da girman ta'asar da wadannan 'yan ta'adda suka aikata.
Janyewar sojoji da 'yan sandan Majalisar Dinkin Duniya a yankin, ya kara dagula al’amura a arewacin kasar da ke fama da rikici, inda sabon rikici ya barke tsakanin sojojin Mali da kungiyoyin 'yan aware.
'Yan awaren dai na zargi sojoji da kawayen su na Wagner da cin zarafin jama'a.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu