Isa ga babban shafi

Yunwa ta kashe mutane a Habasha saboda rashin tallafi

Yunwa ta kashe daruruwan mutane a yankin Tigray bayan da Majalisan Dinkin Duniya da kasar Amurka sun dakatar da tallafin abincin da suke bai wa kasar Habasha. 

'Yan Habasha da suka tserewa rikicin yankin Tigray, yayin da suka yi layin karbar tallafin abinci a sansanin 'yan gudun hijira na Um-Rakoba da ke jihar Al-Qadarif ta kasar Sudan. Ranar 11 ga Disamban, 2020.
'Yan Habasha da suka tserewa rikicin yankin Tigray, yayin da suka yi layin karbar tallafin abinci a sansanin 'yan gudun hijira na Um-Rakoba da ke jihar Al-Qadarif ta kasar Sudan. Ranar 11 ga Disamban, 2020. REUTERS - MOHAMED NURELDIN ABDALLAH
Talla

 

Majalisar Dinkin Duniya da Amurka tun farko sun dakatar da tallafin ne a watan Maris bayan da suka gano kumbiya-kumbaya da ake yi na sace abincin da aka tanadar don mabukata.

Sai dai sun kara tsawaita dakatarwar zuwa wasu sassan Habasaha a watan Yuni, hakan ya shafi mabukata miliyan 20, wato  kashi daya bisa shida na yawan al'ummar kasar.   

Hukumar Jin Kai ta samu rahotanin mace-mace na mutane 728 da ke da alaka da yunwa a uku daga cikin yankuna 7 tun bayan da aka dakatar da tallafin abincin a watan Maris.  

Wannan jawabi wanda kawai hukumomin gundumomi suka tattara ne, kamar yadda shugaban Hukumar Jin Kai ya tabbatar.     

A tsakiyar watan Maris hukumomin bada tallafi na Amurka suka gano abincin tallafi na akalla mutane dubu 134,000 ana sayar wa a kasuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.