Isa ga babban shafi

An kai wa jirgin Turkiyya hari a Sudan

Ma'aikatar tsaron Turkiyya ta bayyana cewa an harbi wani jirgin sojinta da ke aikin kwashe 'yan kasar daga Sudan.

Jirgin saman fasinja na kasar Turkiyya.
Jirgin saman fasinja na kasar Turkiyya. REUTERS - Umit Bektas
Talla

 

An harbi jirgin mai lamba C-130 ne yayin da ya nufi sansanin sojin saman kasar da ke Wadi Seidna domin kwashe 'yan kasar da ke birnin Khartoum, a cewar ma’aikatar.

Sai dai ta ce jirgin ya sauka lafiya, kuma ba bu wanda ya samu rauni a sanadin harbin, kamar yadda kafar yada labaran kasar TRTWorld ta ruwaito.

A yayin da take mayar da martani kan wannan lamari, rundinar sojin Sudan ta zargi dakarun sa-kai na RSF da aikata wannan aika-aika, sai dai RSF din ta musanta hakan.

A wata sanarwa da rundinar ta RSF ta fitar, ta ce “ba gaskiya bane cewa da ake yi mu muka kai wa jigin Turkiyya hari. Tun a daren jiya muka fara mutanta yarjejeniyar da aka yi da mu".

"Ta yaya ma za a ce dakarunmu ne suka kai hari kan jirgin kwashe ‘yan Turkiyya bayan mu ne muka taimaka wurin kare ‘yan kasar a kwanan nan, da ma kwashe sauran ‘yan kasashe a dukkan yankunann babban birnin Sudan".

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.