Isa ga babban shafi

Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta an ci gaba da luguden wuta a Sudan

Ana ci gaba da luguden wuta a birnin Khartoum na kasar Sudan bayan da sojojin kasar suka ayyana tsagaita bude wuta na tsawon kwanaki uku, kuma ba a san tushen harbe-harben ba, kamar kamfanin dillancin labarai na Reuters ya tabbatar.

Yadda hayaki ya turnuke sararin a birnin Khartoum na kasar Sudan kenan.
Yadda hayaki ya turnuke sararin a birnin Khartoum na kasar Sudan kenan. © INSTAGRAM @LOSTSHMI via REUTERS
Talla

Haka zalika ana ci gaba da jiyo amon harbe-harbe da kuma fashewar nakiya a wasu wurare.

Rundunar sojin Sudan ta ce ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta ta tsawon kwanaki uku, domin baiwa al'ummar Sudan damar gudanar da bukukuwan karamar Sallah, bayan kawo karshen azumin watan Ramadan.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce dakarun sojin kasar na fatan 'yan tawayen za su bi dukkan sharuddan tsagaita bude wuta da kuma dakatar da duk wani yunkuri na soji da zai kawo mata cikas.

A ranar Juma'a ne dakarun kai daukin gaggawa na musamman suka fara fafatawa da sojoji a fadin kasar Sudan kusan mako guda.

Ko da yake rundunar da ke biyayya ga mataimakin shugaban gwamnatin mulkin sojin kasar, Janar Mohammed Hamdan Dagalo ta amince da yarjejeniyar tsagaita wutar ta tsawon sa’o’I 72.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.