Hukumar INEC ta yi barazanar gurfanar da jam’iyyar PDP a gaban kotu
Hukumar Zaben Najeriya INEC ta yi barazanar gurfanar da babbar jam’iyyar adawa ta PDP a gaban kotu, bisa zargin bata sunan shugaban hukumar Farfesa Mahmoud Yakubu.
Wallafawa ranar:
Sakataren yada labaran hukumar Mr Rotimi Lawrence Oyekanmi ne ya bayyana wannan barzana a birnin tarayyar kasar Abuja.
A cewar sa jam’iyyar PDP na yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da bata sunan shugaban hukumar ta hanyar zargin sa da magudi a zaben da ya gabata da kuma saura tsarin na’urar tantance masu zabe ta BVAS da gangan kawai don samun nasarar jam’iyyar APC.Ya ce bayan kiraye-kirayen sallamar shugaban hukumar da PDP ke yi, da kuma maka ta a kotyu bisa zargin hada kai da magudi, jam’iyyar na kuma ci gaba da bata sunan shugaban hukumar a idanun duniya da angiza ‘yan Najeriya kan su tsane shi ko ma kai masa hari.
Wannan ta sa a cewar sa donle ne hukumar ta dauki matakin shari’a a kan jam’iyyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu