Isa ga babban shafi

Somalia: Wani abu ya fashe a kusa da ofishin magaajin garin Mogadishu

Fashewar wani abu kusa da ofishin magajin garin Mogadishu a tsakiyar birnin ya  lalata gine gine a Lahadin nan, inda daga bisani aka kaure da musayar wuta a  tsakanin dakarun gwamnatin Somalia  da na kungiyar Al-Shabaab, wadda tuni ta dau alhakin harin.

Mayakan al-Shabaab suna ci gaba da kai hare hare Mogadishu, babban birnin Somalia.
Mayakan al-Shabaab suna ci gaba da kai hare hare Mogadishu, babban birnin Somalia. AFP
Talla

Wani babban jami’in ‘yan sanda a birnin, Abdullahi Mohamed ya  ce ‘yan ta’addan sun yi amfani da wata mota ce da suka makare da abubuwa masu fashewa  wajen kai harin.

Ganau sun ce fashewar ta lalata gine ginen da ke kusa da wurin, kuma har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, ana iya jin karar musayar wuta daf da ofishin magajin garin na birnin Mogadishu.

Sun ce an samu wadanda abin ya rutsa da su, amma jami’an tsaron sun yi wa yankin kawanya, tare da umurnin cewa kowa ya bar wurin.

Kungiyar Al-Shabaab, mai alaka da Al-Qaeda ta dau alhakin wannan harin ta wata tashar sadarwarta, tana mai cewa mayakanta sun kutsa cikin ginin da suka kai harin bayan da suka kasha masu gadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.