Isa ga babban shafi

Yunwa ce ke tilasta wa 'yan mata zaman daduro a Ghana

Wani bincike ya nuna cewa, yunwa da talauci na tilasta wa 'yan mata masu kananan shekaru zaman daduro da samarinsu a Ghana, yayin da wasu 'yan matan ake yi musu auren dole saboda gudun cikin-shege.

In Ghana, a light -skinned woman applies a bleaching soap on her  face with the hope of lightening her complexion.
In Ghana, a light -skinned woman applies a bleaching soap on her face with the hope of lightening her complexion. © RFI/Pearl Akanya Ofori
Talla

Binciken da hukumar GSS ta gudanar  ya nuna cewa, akalla 'yan mata dubu 80 ne ke irin wannan zaman na daduro da kuma auren dole a fadin Ghana, kuma shekarunsu bai wuce tsakanin 12 zuwa 17 ba.

Wasu daga cikin iyayen yaran sun ce, gudun kada 'ya'yansu su kawo musu cikin shege gida ne ya sa suke aurar da su da wuri.

Daya daga cikin 'yan matan da muka zanta da su ta ce, lallai talauci ne ya sa take zaman daduro da saurayinta wanda ta ce, yana ba ta abincin safe da rana da dare.

Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken rahoton daga wakilinmu Abdallah Sham'un Bako

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.