Isa ga babban shafi

Kenya ta aika da sojoji zuwa Congo domin yakar 'yan tawaye - Ruto

Shugaban kasar Kenya William Ruto ya sanar da cewa, kasarsa na shirin tura dakaru zuwa gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, a wani shirin hadin gwiwa na yaki da 'yan tawaye.

Shugaban Kenya kenan, William Ruto
Shugaban Kenya kenan, William Ruto REUTERS - MONICAH MWANGI
Talla

Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango mai arzikin ma'adinai na fafutukar ganin ta shawo kan kungiyoyin da ke dauke da makamai da dama wadanda ci gaban da suka samu a gabashin kasar a baya-bayan nan ya sake farfado da tsohuwar gaba tare da haifar da tashin hankali da makwabciyarta Ruwanda.

Shugabannin kungiyar kasashen gabashin Afirka bakwai da Kenya ke jagoranta, sun amince a watan Afrilu na kafa rundunar hadin gwiwa da za ta taimaka wajen dawo da tsaro a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango.

Da yake magana a wajen wani biki da aka yi a Nairobi na kaddamar da tura sojojin, Ruto ya ce an tura sojojin ne domin kare rayukan fararen hula.

Kenya ce za ta jagoranci rundunar, wanda kuma zai hada da sojoji daga Burundi, Sudan ta Kudu da Uganda.

Za a jibge dakaru na Rwanda a kan iyakar kasar, bayan da Kinshasa ta nuna adawa da da kasancewar gwamnatin Kigali cikin shirin na wanzar da zaman lafiya a Congo ba.

Rundunar sojin Kenya ta ce za a jibge rundunar na tsawon watanni shida, kuma za ta kafa sansanin kwamandojin ta a Goma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.