MDD ta gano yadda ma'aikata suka rungumi rashawa a Ghana
Wani bincike da hukumar kula da nagartar ma'aikata ta kasar ghana ta gudanar ya gano cewa kimanin kudin kasar CEDI biliyan biyar aka bayar a matsayin cin hanci ga ma'aikatan kasar.
Wallafawa ranar:
Kunna - 02:59
Binciken da hukumar ta gudanar tare da hadin gwiwar Majalisar dinkin Duniya ya bayyana yadda kudade ke salwanta da sunan cin hanci, duk da ikirarin da gwamnati ke yi na kawo karshen matsalar.
An dai gudanar da wannan bincike ne domin gano yadda wannan matsala ke ciwa al'ummar kasar tuwo a kwarya, duk da irin matakan da gwamnati ke cewa tana dauka a kai.
Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron rahoton wakilinmu daga birnin Accra na kasar Ghana, Abdallah Sham'un Bako.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu