Isa ga babban shafi

'Yan bindiga sun kashe mutane 19 a Afirka ta Kudu

‘Yan sandan Afirka ta Kudu sun ce hare-haren bindiga kashi biyu, a wani gari kusa da birnin Johannesburg, da kuma wani a gabashin kasar, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 19.

Mutane sun taru a wurin da 'yan bindiga suka harbe mutane da dama a wata mashaya cikin dare a garin Soweto, Afirka ta Kudu.10 ga Yuli, 2022.
Mutane sun taru a wurin da 'yan bindiga suka harbe mutane da dama a wata mashaya cikin dare a garin Soweto, Afirka ta Kudu.10 ga Yuli, 2022. AP - Shiraaz Mohamed
Talla

A cikin sanrwar da suka fitar a yau Lahadi, ‘yan sanda sun ce, a garin Soweto, mutane 15 aka kashe a lokacin da suke  shakatawa cikin dare, lokacin da maharan da suka isa mashayar cikin karamar motar bas suka bude wuta kan mutanen dake wurin.

A gabashin birnin Pietermaritzburg kuwa, jami’an tsaro sun ce mutane hudu suka mutu, wasu takwas kuma. suka jikkata, bayanda wasu ‘yan bindiga biyu suka budewa wuta kan mutane dake shakatawa a wata mashaya.

Majiyoyin 'yan sanda sun ce ya yi wuri a alakanta hare-haren biyu, said ai babu shakkah kan kamanceceniyar da suka yi da juna.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.