Isa ga babban shafi

Cote d'Ivoire ta ware dala miliyan 405 don kange barazanar 'yan ta'adda

Gwamnatin Cote d’Ivoire ta sanar da ware dala milyan 405 domin karfafa tsaro a kan iyakar kasar da Burkina Faso da kuma Mali wadanda ke fama da ayyukan ta’addanci.

Shugaban Cote d'Ivoire, Alassane Ouattara na zantawa da  RFI.
Shugaban Cote d'Ivoire, Alassane Ouattara na zantawa da RFI. RFI
Talla

Mamadou Touré, ministan samar wa matasan kasar ayyukan yi, ya ce za a yi amfani da wadannan kudade ne wajen samar wa matasa ayyukan yi, wanda zai hana su mara wa ayyukan ta’addanci baya.

Tun bayan tsanantar ayyukan ta'addanci a makwabtanta, gwamnatin Cote d'Ivoire ta daura damarar wayar da kan matasa da nufin hana su shiga makamantan ayyukan.

Haka zalika ma'aikatar tsaro ta karfafa jami'an tsaro a kan iyakokin kasashen 2 baya ga tsananta bincike kan duk da wani zargi kan daidaikun mutane ko kuma kungiyoyi duk dai a kokarin hana fantsamuwar kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.