Isa ga babban shafi

Nakiya ta kashe wani sojin Majalisar Dinkin Duniya a Mali

Wani jami’in rundunar kiyaye zaman lafiya ta majalisar dinkin duniya  ya mutu bayan da ya taka nakiya a arewacin Mali da ke fama da rikici  a yau Lahadi, a yayin da yake sintiri a yankin, kamar yadda shugaban rundunar ta MINUSMA a Mali ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Wasu dakarun MINUSMA a yankin Gao na Mali.
Wasu dakarun MINUSMA a yankin Gao na Mali. Minusma/Harandane Dicko
Talla

Jami’in kiyaye zaman lafiyar wanda yake daga cikin tawagar sojin kasar Guinea da ke aiki da dakaru na musamman ya ji rauni ne da farko, daga bisani ya mutu a asibiti a garin Kidal.

Wanann hatsari na zuwa ne a daidai lokacin da ake tattaunawa mai cike da tankiya a kan sabanta zaman rundunar ta MINUSMA a Mali.

Jimillar dakarun kiyaye zaman lafiya na rundunar MINUSMA 175 ne suka mutu sakamkon rikicin da ake a Mali.

Rikicinn Mali ya yi sanadin mutuwar dubban daruruwan mutane, tare da daidaita da dama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.