Isa ga babban shafi

'Yan tawayen Chadi sun yi kira da a saki 'yan adawa da aka tsare

Kungiyoyin 'yan tawayen kasar Chadi sun yi kira da a gaggauta sako gungun 'yan adawar da aka kama a farkon wannan wata sakamakon zanga-zangar kin jinin Faransa.

Wasu masu zanga-zanga da ke kone tutar Faransa à Ndjamena, 14/05/22.
Wasu masu zanga-zanga da ke kone tutar Faransa à Ndjamena, 14/05/22. © AFP
Talla

Kungiyoyin 'yan tawayen sun yi kira da a gaggauta sakinsu ba tare da wani sharadi ba a wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar.

A ranar litinin, da ta gabata hukumomin Chadi sun tuhumi wasu jiga-jigan jam'iyyar adawa ta Wakit Tamma da laifin cin zarafin jama'a sakamakon zanga-zangar da suka shirya ranar 14 ga watan Mayu wanda ta kaiga tsare su.

An tsare kodinetan Wakit Tamma, Max Loalngar, kuma an gurfanar da shi a gaban kotu a ranar Alhamis, saidai  an dage sauraron shari’ar nasu har zuwa ranar 6 ga watan Yuni.

Zanga-zangar ta shafi Faransa ne, wadda masu fafutuka ke zargin tana goyon bayan gwamnatin mulkin soja a Chadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.