Isa ga babban shafi

An yi artabu tsakanin magoya bayan jagororin Libya

Rikici ya barke a babban birnin Tripoli na Libya tsakanin magoya bayan bangarorin da ke muliki a kasar a wannan Talatar, inda suka shafe tswon sa’o’i suna artabu.

Rikicin ya barke ne gabanin bullowar alfijir
Rikicin ya barke ne gabanin bullowar alfijir REUTERS - OMAR IBRAHIM
Talla

Kawo yanzu babu bayanai game da irin barnar da wannan arangama ta haddasa tsakanin bangarorin biyu da basa-ga-maciji a kasar ta Libya mai arzikin man fetur.

Libya dai ta jima karkashin mulkin Firaminista Abdulhamid  Dbeibah, amma ya fuskanci kalubale daga Fathi Bashaga, da Majalisar Dokoki ta ayyana a matsayin wani Firaministan na daban a cikin watan Fabairu a yankin gabashin kasar, inda kuma ya samu goyon bayan Khalifa Haftar.

Rikicin dai ya barke ne tun ma gabanin bullowar alfijir bayan da jami’an yada labarai na Firaminista Bashaga suka sanar da isowarsa birnin Tripoli cikin rakiyar wasu ministocinsa domin fara aiwatar da wani aiki.

Ana fargabar cewa, wannan sabon tashin hankalin zai sake haddasa makamancin rikicin da aka gani a 2011 bayan Kungiyar Tsaro ta NATO ta goyi bayan juyin juya halin da ya yi sanadiyar kifar da gwamnatin Moammar Gaddafi da kuma fadan da ya barke a 2019-2020, lokacin da magoya bayan Haftar suka kai hari a babban birnin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.