Isa ga babban shafi
Burkina Faso - Ta'addanci

Harin ta'addanci a sansanin soji ya lakume dakarun Burkina faso 5

Kimanin mutane 10, ciki har da sojoji 5 ne suka mutu a wani hari da aka kai wa wata cibiyar soji a Burkina Faso a yau Lahadi.

Taswirar Burkina Faso.
Taswirar Burkina Faso. © RFI
Talla

Wata majiyar tsaro ta shaida wa kamfani dillancin labaran Faransa cewa da misalin karfe 5 na asubahin yau wata kungiyar ‘yan ta’adda ta kai farmaki kan sansanin sojin Gaskinde a lardin Soum, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 10.

Majiyar ta ce saura wadanda suka mutu fararen hula ne, kana daga bisani wani jami’in gwamnati a yankin ya tabbatar da mutuwar fararen hula 4.

Kungiyoyi masu ikirarin jihadi da ke da alaka da Al-Qaeda da kungiyar IS sun yi ta kaddamar da hare hare a arewaci da gabashin Burkina Faso tun daga shekarar 2015, abin da ya yi sanadin mutuwar sama da mutane dubu 2 tare da daidaita kusan miliyan 2.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.