Isa ga babban shafi
Algeria-Morocco-Spain

Algeria ta janye jakadanta na Spain

Algeria ta umurci jakadanta na kasar Spain ya  dawo gida biyo bayan shawarar kasar ta bada goyon baya ga shirin da Morocco ke yi na bada ikon cin gashin kai  ga yankin Arewacin Sahara da ake rikici a kai a karkashin kasarta.

Shugaban Algeria, Abdelmadjid Tebboune.
Shugaban Algeria, Abdelmadjid Tebboune. © France24 screengrab
Talla

Wata sanarwa daga ma’aikatar harkokin wajen kasar, ta yi tir da Spain, wadda kafin yanzu  bata nuna goyon baya ga kowane bangare ba a kan rikicin da aka shafe gwamman shekaru ana yi tsakanin Morocco da Algeria a kan yankin na Arewacin sahara.

A ranar Juma’a ce  ministan harkokin wajen Spain, Jose Manuel Albares ya bayyana matakin gwamnatin kasarsa na goyon  bayan Morocco a kan  bada kwarya kwaryar ikon cin gashin kai  ga Arewacin Saharar a karkashinta

Algeria ta bayyana kaduwarta a game da sauyin manufa da Spain ta yi, ta wajen bada goyon baya ga Morocco a kan wannan rashin jituwa tsakanin kasashen biyu na yankin arewacin Afrika.

Kungiyar  Polisario da ke fafutukar neman yancin arewacin Saharar ta mayar da martini cikin fushi ga sanarwar Spain, tana mai kira da a matsa mata lamba har sai ta sauya ra’ayinta.

Kungiyar ta yi kira da a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta da majalisar dinkin duniya ta taimaka aka cimma a shekarar 1991, wadda ya tanadi cewa za a gudanar da zaben raba gardama a kan idonta, a game da batun samun yancin kai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.