Isa ga babban shafi
Mauritius

Mahaukaciyar Iska Da Ruwan Sama Sun tsugunar da Harkoki a Mauritius

A kasar Mauritius dubban gidaje  suka rasa hasken wutan lantarki bayan da mahaukaciyar iska da ruwan sama suka ratsa kasar.

The cyclone pounded Mauritius with heavy downpours and winds of 120 kilometres per hour, with a peak of 151 kilometres per hour recorded in the capital Port Louis
The cyclone pounded Mauritius with heavy downpours and winds of 120 kilometres per hour, with a peak of 151 kilometres per hour recorded in the capital Port Louis Laura MOROSOLI AFP
Talla

Mahaukaciyar iska da ruwan saman da suka rika gudun kilomita  130 cikin sa’a  guda sun yi barnar gaske a babban birnin kasar Port Louis.

Wannan mahaukaciyar iska da goguwa da ruwan sama sun tsaida dukkan harkokin yau da kullum a fadin kasar.

Hukumomi na cewa gidaje akalla 7,500 babu hasken wutan lantarki bayan da iska da itatuwa suka  karya turakun wayoyin lantarki.

Kazalika wayoyin sadarwa sun fuskanci matsala sakamakon iska.

A shekara ta 2007 mutane biyu suka rasa rayukansu sakamakon irin wannan mahaukaciyar  iska da ruwan sama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.