Isa ga babban shafi
Libya-Zaben Libya

Kasashen duniya na dakon ranar zaben Libya

Amurka da wasu manyan kasashen Turai sun bukaci Libya da ta gaggauta tsayar da sabuwar ranar gudanar da zaben shugabancin kasar da aka jinkirta.

Seif al-Islam Kadhafi, da ga marigayi Mu'ammar Gaddafi na cikin masu neman kujerar shugabancin Libya
Seif al-Islam Kadhafi, da ga marigayi Mu'ammar Gaddafi na cikin masu neman kujerar shugabancin Libya STRINGER libyan High National Electoral Comission FB Page/AFP/File
Talla

A cikin wata sanarwar hadin-guiwa da kasashen suka fitar, sun roki jagororin  Libya da su fitar da jerin sunayen karshe na ‘yan takarar shugabancin kasar.

Tun da fari,  hukumomin da ke sanya ido kan zaben na Libya sun ce, mawuyaci ne a gudanar da zaben a jiya Juma’a kamar yadda aka tsara da farko.

Yanzu haka masu shirya zaben na duba yiwuwar gudanar da shi a ranar 24 ga watan Janairu mai zuwa, amma ana ganin da wahala sauran bangarorin kasar su amince da wannan rana.

Ana sa ran wannan zaben zai bude sabon babin rayuwa ga kasar ta Libya wadda ta kwashe tsawon shekaru tana fama da rikice-rikice.

Rikicin ya samo asali ne tun bayan da aka kashe tsohon shugaban kasar Mo’ammar Gaddafi a shekarar 2011 a wani juyin mulki da aka yi masa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.