Isa ga babban shafi
Kenya

Manyan 'yan ta'adda sun tsere daga gidan yarin Kenya

Rundunar ‘yan sandan Kenya ta ce, manyan ‘yan ta’adda uku sun tsere daga wani gidan yarin kasasr ciki har da wanda aka yanke wa hukuncin daurin shekaru 41 saboda samun shi da laifi a harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 148.

Jami'an tsaron Kenya
Jami'an tsaron Kenya AFP/File
Talla

Sashen binciken manyan laifufuka a rundunar ‘yan sandan kasar ya sanar da ware Dala dubu 535 ga duk wanda ya taimaka da bayanai don cafke  mutanen wato Mohamed Ali Abikar, Joseph Juma Odhiambo da kuma Musharaf Abdalla Akhulunga da suka tsere daga gidan yarin mafi tsaro a kasar da ake kira Kamiti a wajen birnin Nairobi.

Hukumomin Kenya ba su yi bayani ba kan yadda manyan ‘yan ta’addan suka tsere daga gidan yarin na Kamiti mai cike da tsaro.

Kodayake Kwaminishinan Kula da Gidajen Yarin kasar, Wycliffe Ogallo ya ce, ya ziyarci gidan kason domin tantance yadda ‘yan ta’addan suka tsere.

Ogallo ya gargadi jama’a da su kauce wa samar da matsugumi ga wadannan mutane masu cike da hadari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.