Isa ga babban shafi
ECOWAS - Guinea

Tsohon shugaban Guinea na cikin koshin lafiya - ECOWAS

Wakilan kungiyar kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS sun ce, hambararren shugaban kasar Guinea Alpha Conde na cikin koshin lafiya.

Tsohon shugaban kasar Guinea Alpha Conde.
Tsohon shugaban kasar Guinea Alpha Conde. AFP/File
Talla

Wakilan tawagar ta ECOWAS sun bada tabbacin ne  yayin ziyarar da suka fara a kasar jiya Juma’a don ganawa da sojojin da suka yi juyin mulki a karkashin Lafatanar Kanal Mamady Dambouya.

A makon da ya kare ne dai kungiyar kasashen na yammacin Afirka ta dakatar da Guinea daga cikinta, yayin da kuma a Juma’ar nan, kungiyar kasashen Afirka AU ta bi sahu.

Shugaban Hukumar Gudanarwar ECOWAS Jean-Claude Kassi Brou, wanda ke cikin tawagar da ta sauka a birnin Conakry, ya ce masu shiga tsakani sun gana da tsohon shugaba Conde kuma yana samun kulawa mai kyau.

Juyin mulkin da aka yi a Guinea dai shi ne na 4 cikin watanni 13 a Yammaci da kuma Tsakiyar Afirka, abin da ya tayar da hankalin masu sa ido kan yadda gwamnatocin da sojoji ke jagoranta ke karuwa a yankunan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.