'Yan tawaye sun kona fararen hula 19 har lahira a Congo
Hukumomi a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo sun ce Fararen hula 19 ne ‘yan tawayen Uganda suka daddatse tare da kone su har lahira.
Wallafawa ranar:
An tsinci gawarwaki 14 a ranar Asabar, kwana guda bayan aukuwar lamarin, kamar yanda kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito.
Wani basaraken yanki ya ce jami’an kungiyar agaji ta Red Cross ne suka gano gawarwakin a yayin da suka shiga daji don neman wadanda suka bace a yayin harin da aka kai kauyen Kasanzi da ke yankin Beni a arewacin Kivu.
Beni na tsakiyar yankin da kungiyar ‘yan tawaye ta Allied Democratic Forces (ADF), mai nasaba da ISIS ta ke kai munanan hare hare duk matakin dokar ta baci da shugaba Felix Tshisekedi ya dauka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu