Isa ga babban shafi
Chadi

Rikicin manoma da makiyaya ya lakume rayukan mutane 22

Hukumomin kasar Chadi sun ce mutane akalla 22 suka rasa rayukansu a kasar, sakamakon fadan da ya barke tsakanin wasu manoma da makiyaya a ranar Lahadi.

Rikici tsakanin manoma da makiyaya a Chadi ya dade yana janyo hasarar rayukan da dimbin dukiya.
Rikici tsakanin manoma da makiyaya a Chadi ya dade yana janyo hasarar rayukan da dimbin dukiya. © AFP
Talla

Gwamnan lardin Hadjer-Lamis Amina Kodjiana ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, rikicin ya samo asali ne kan mallakar filaye tsakanin bangarorin biyu a kauyen Zohana mai nisan kilomita akalla 200 daga birnin N’Djemena.

Gwamnar ta ce wasu mutane 18 sun jikkata a tashin hankalin, yayin da kakakin gwamnatin Chadi Abdramane Koumallah yace an tura karin sojoji wurin domin tabbatar da tsaro.

Rikici tsakanin manoma da makiyaya a yankin Sahel ya dade yana haifar da tashin hankalin da ke lakume rayuka da dama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.