Isa ga babban shafi
Tunisia - 'Yan Ci Rani

'Yan ci rani 43 sun nutse a gabar ruwan Tunisia

Jami’an agaji a Tunisia sun sanar da bacewar akalla mutane 43 sakamakon kifewar wani jirgin ruwa dauke ‘yan ci rani 127 a gabar ruwan kasar dake yankin kudu maso gabashi.

Jami'an tsaron gabar ruwan Tunisia tsaye a kusa da gawarwakin wasu 'yan ci rani da aka tsamo daga teku a garin Sfax dake yankin tsakiyar kasar ta Tunisia.
Jami'an tsaron gabar ruwan Tunisia tsaye a kusa da gawarwakin wasu 'yan ci rani da aka tsamo daga teku a garin Sfax dake yankin tsakiyar kasar ta Tunisia. AP - Houssem Zouari
Talla

Kungiyar agajin gaggawa ta Red Crescent dake kasar ta Tunisia ta ce an samu nasarar ceto 84 daga cikin ‘yan ci ranin da suka nutse, yayin da har yanzu ake laluben ragowar 43.

Bayanai sun ce ‘yan ci ranin dake neman. tsalaka teku zuwa nahiyar Turai sun fito ne daga kasashen Chadi, Eritrea, Sudan, Masar da kuma Bangladesh.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.