Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Dimokaradiyar Congo

Congo ta nemi afuwa kan shelar yiwuwar sake aman wutar tsauni

Gwamnatin Jamhuriyar Dimokaradiyar Congo ta nemi afuwa bisa kuskuren da ta yi na yin shelar gargadin yiwuwar sake fuskantar aman wuta daga tsaunin Nyiragongo a ranar Juma’a.

Masu motoci da Babura a kan narkaken dutsen da ya bushe bayan aman wutar da tsaunin Nyiragongo a gaf da Goma, babban birnin lardin arewacin Kivu.
Masu motoci da Babura a kan narkaken dutsen da ya bushe bayan aman wutar da tsaunin Nyiragongo a gaf da Goma, babban birnin lardin arewacin Kivu. © AFP
Talla

Gargadin na jiya dai ya firgita jama’a abinda ya sanya mutane kusan dubu 400 tserewa daga birnin Goma dake kusa da tsaunin mai aman wutar.

A makon da ya gabata tsaunin Nyiragongo ya yi aman wuta mai kunshe da narkaken dutsen da yayi  sanadin mutuwar mutane akalla 12 duk da aikin kwashe dubban jama'ar da aka yi daga yankunan dake kusa da shi.

Yayin da kuma kididdigar da aka yi ta nuna sai da iftila’in aman wutar hade da narkakken dutsen ya lakume gidaje kimanin gidaje dubu 20 kafin ya tsaya a gaf da birnin Goma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.