Isa ga babban shafi
ECOWAS - Mali

ECOWAS za ta yi taron gaggawa kan rikicin siyasar Mali

Shugabannin kasashen dake kungiyar ECOWAS za su gudanar da wani taron gaggawa ranar lahadi mai zuwa domin tattauna rikicin siyasar kasar Mali sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi wajen kawar da gwamnatin rikon kwaryar kasar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan dake zama babban Jakadan kungiyar ECOWAS a kokarin sasanta rikicin siyasar kasar Mali.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan dake zama babban Jakadan kungiyar ECOWAS a kokarin sasanta rikicin siyasar kasar Mali. © Presidency of Nigeria
Talla

Kungiyar tayi barazanar sake sanyawa kasar Mali takunkumi sakamakon juyin mulkin wanda ya kawo karshe shirin mika mulki ga fararen hula a shekara mai zuwa.

Shugaban rikon kwaryar kasar Bah Ndaw da Firaministan sa Moctar Ouane sun aje mukaman su bayan tsare su da sojoji suka yi, yayin da shugaban sojin Assimi Goita ya bayyana kan sa a matsayin jagoran sabuwar gwamnatin sojin.

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan jakadan ECOWAS na sasanta rikicin Mali, yayin ganawa da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da sauran mukarrabansa a fadar gwamnati dake birnin Abuja.
Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan jakadan ECOWAS na sasanta rikicin Mali, yayin ganawa da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da sauran mukarrabansa a fadar gwamnati dake birnin Abuja. © Presidency / Femi Adesina

Tawagar kungiyar ECOWAS a karkashin jagorancin tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ta ziyarci Mali inda ta gana da sojojin da kuma shugabannin da aka tube.

Tuni Jonathan ya koma Najeriya inda ya gabatar da rahotan ziyarar sa ga shugaba Muhammadu Buhari kafin taron da zai gudana a karshen wannan mako.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.