Isa ga babban shafi
Tunisia - Coronavirus

Al'ummar Tunisia sun koma karkashin dokar kulle saboda Korona

Gwamnatin Tunusia ta kafa dokar takaita zirga-zirgar jama’a a daukacin kasar da ta ce ta soma aiki daga yau Lahadi har tsawon mako 1, domin dakile yaduwar annobar Korona.

Yadda wani sashin birnin Tunis ya kasance jim kadan bayan soma aikin sabuwar dokar kullen wucin gadi domin dakile yaduwar annobar Korona.
Yadda wani sashin birnin Tunis ya kasance jim kadan bayan soma aikin sabuwar dokar kullen wucin gadi domin dakile yaduwar annobar Korona. AP - Hassene Dridi
Talla

Yayin sanar da matakin, Fira Ministan Tunisia Hichem Mechichi ya ce kafa dokar kullen ta wucin gadi ya zama dole, ganin yadda annobar ke barazanar durkusar da asibitoci da sauran cibiyoyin kula da lafiyar kasar, a daidai lokacin da cutar ke lakume rayukan akalla mutane 100 a kowace rana.

Fira Ministan ya kara da cewar yanzu haka Tunusia na fuskantar kalubale mafi muni a fannin kula da lafiyar ‘yan kasar.

A karkashin sabuwar dokar kulle ta Tunusia, Masallatai, manyan kasuwanni da za su kasance a rufe tsawon makon guda, zalika an haramta tafiye-tafiye tsakanin yankuna, an hana taruka da sauran nau’kan bukukuwa, sai  kuma haramta fitar da aka yi tsakanin karfe 7 na dare zuwa 5 na safe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.