Isa ga babban shafi
Zaben - Nijar

Manyan 'yan siyasa 2 su na fafatawa a zagaye na 2 a zaben Nijar

A yayin da al’ummar Jamhuriyar Nijar, suka soma kada kuri'a a zagaye na 2  na zaben shugaban kasa, za suyi zabi ne tsakanin manyan ‘yan siyasa masu fada a ji 2, a zaben shugaban kasa, zagaye na 2 a yau Lahadi, a kokarinsu na tabbatar da mika mulki daga hannun farar hula zuwa farar hula a karon farko a tarihin kasar da juyin mulki ya wa katutu.

Bazoum Mohammed da abokin takarar sa Mahamane Ousmane
Bazoum Mohammed da abokin takarar sa Mahamane Ousmane RFI Hausa
Talla

Daga cikin al’ummar kasar miliyan 22,miliyan 7 da dubu dari 4 ne kawai suka cancanci kada kuri’a a yaau Lahadi, sauran kuwa, ba su kai munzulin kada kuri’a ba.

Dubban sojoji ne aka girka a sassan kasar don tabbatar da tsaro a yayin kada kuri’ar a kasar da ke kan hanyar mika mulki cikin lumana tsakanin daga zababben shugaba daa wa’adinsa mulkinsa ya cika, zuwa wani zababben shugaban, a karon farko tun da kasar ta samu yancin mulkin kai daga turawan mulkin mallaka na Faransa a shekarr 1960.

An yi na’am da shawarar shugaban Nijar mai barin gado, Mahamadou Issoufou na sauka daga karagar mulki, bayan cikar wa’adin mulki 2na shekaru 5 kowanne a nahiyar da shugabanni da dama suka yi kokarin yin kane kane a kan madafun iko.

Magajinsa zai kasance na hannun damarsa kuma wanda yake goyon baya, Mohamed Bazoum ko Mahamane Ousmane, wanda ya kasance zababben shugaban kasar na farko a shekarar 1993, sojoji suka hambarar da shi bayan shekaru 3.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.