Isa ga babban shafi
Najeriya-Kamaru

Najeriya ta fara shirin kwashe ‘yan kasar ta dake gudun hijira a Kamaru

Gwamnatin Najeriya ta fara shirin kwashe ‘yan kasar ta dake gudun hijira a Kamaru domin mayar dasu gida, bayan da jami’an kasashen 2 suka tattauna kan shirin karkashin Majalisar Dinkin Duniya a birnin Marwa.

'Yan Najeriya dake sansanin 'yan gudun hijira na Minawao dake yankin arewa mai nisa a kasar Kamaru.
'Yan Najeriya dake sansanin 'yan gudun hijira na Minawao dake yankin arewa mai nisa a kasar Kamaru. © NHCR/D.Mbaiorem
Talla

Kwamishinan kula da ‘yan gudun hijira a Najeriya Sanata Bashir Garba Lado yace taron ya biyo bayan umurnin shugaban kasa Muhammadu Buhari na ganin an kwashe ‘yan gudun hijirar dake zama a Kamaru cikin gaggawa.

Takwaransa dake Kamaru Tai Hassan Ejibunu ya yaba da tattaunawar da aka yi tsakanin bangarorin uku wanda yace za’ayi aikin ne wajen kwashe bakin dake bukatar komawa gida.

Taron yace shirin dawo da yan gudun hijirar ya kunshi samar musu da matsuguni, inda za’a basu gidaje masu dakuna bibbiyu a wasu jihohin kasar dake kusa da cibiyoyin kula da lafiya da makarantu da wuraren koyon sana’oi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.