Isa ga babban shafi
Habasha

'Yan tawayen Tigray sun yi barazanar kaiwa Eritrea farmaki

Jam’iyyar TPLF mai mulkin yankin Tigray da ta bijirewa gwamnatin Habasha, ta dauki alhakin jerin hare-haren makaman roka da ta aka kaiwa wasu filayen jiragen sama dake gaf da yankin.

Wasu daga cikin 'yan Habasha mazauna yankin Tigray da suka tserewa muhallansu sakamakon fadan da ake gwabzawa tsaknin sojoji da 'yan tawayen jam'iyyar TPLF
Wasu daga cikin 'yan Habasha mazauna yankin Tigray da suka tserewa muhallansu sakamakon fadan da ake gwabzawa tsaknin sojoji da 'yan tawayen jam'iyyar TPLF AFP
Talla

Daya daga cikin jagororin jam’iyyar ta TPLF Getachew Reda ya ce sun kai farmakin ne da zummar dakile shirye-shiryen dakarun Habasha na kai musu farmaki daga sansanoninsu dake yankunan Massawa da Asmara a kasar Eritrea dake makwabtaka da yankin na Tigray a kasar ta Habasha.

‘Yan tawayen na Tigray sun kuma yi barazanar kaddamar da hare-hare kan wasu yankunan kasar Eritrea da suka yi iyaka da ita, muddin ta cigaba da baiwa dakarun Habasha damar kafa sansanoninsu a kasar.

A karshen makon nan majalisar dinkin duniya ta yi gargadin yiwuwar tafka laifukan yaki a yankin Tigray na Habasha, inda a yanzu haka ake gwabza fada tsakanin sojojin kasar da kuma ‘yan tawayen da ke marawa jam’iyyar TPLF mai mulkin yankin da ta bijirewa gwamnati.

A makon jiya Fira Ministan Habasha Abiy Ahmed ya bada umarnin kaddamar da farmakin soji kan mayakan sa kan na Tigray, bayada ya tuhumi shugabannin yankin da yunkurin haifar tashin hankali a kasar, ta hanyar daukar nauyin horas da mayaka tare da basu makamai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.