Isa ga babban shafi
Afrika

Shugabannin Afrika za su yi tattaunawar sulhu a Mali

Shugabannin kasashen Afrika 5 na kan hanyarsu ta zuwa Bamako na kasar Mali domin shiga tattaunawar sulhu da ake ci gaba da yi a kasar.

Shugaban Mali Ibrahim Boubacar Keïta na fuskantar gagarumin matsin lamba daga bangaren 'yan adawa da ke son ya yi murabus.
Shugaban Mali Ibrahim Boubacar Keïta na fuskantar gagarumin matsin lamba daga bangaren 'yan adawa da ke son ya yi murabus. REUTERS/Michele Tantussi
Talla

Shugabannin 5 sun hada da na Ivory Coast da Ghana da Senegal da  Nijar, wadanda ake sa ran su shiga tattaunawar a Bamako a ranar Alhamis.

Shugaban Mali Boubakar Keita na fuskantar matsin lamba tun watan jiya daga masu bore da ‘yan adawa da ke neman ya yi murabus saboda rashin tsaro da matsalar cin hanci da gazawa wajen tada komadar tattalin arzikin kasar.

Mutane 11 aka tabbatar da mutuwarsu saboda boren ya zuwa yanzu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.