Isa ga babban shafi
Najeriya

Musayar makamai da shanu a Zamfara

Gwamnan Zamfara dake Najeriya, Bello Matawalle, ya yi alkawarin bayarda shanu biyu a matsayin musaya ga duk dan bindigar da ya mika bindigarsa ta AK47 a jihar.

Wasu daga cikin yan bindiga da suka dau niyar ajiye makamai
Wasu daga cikin yan bindiga da suka dau niyar ajiye makamai REUTERS/Goran Tomasevic/File Photo
Talla

Gwamna Matawalle ya bayyana haka ne a alhamis din nan, lokacin da ya karbi bakuncin babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Muhd Adamu da kuma shugaban hukumar jami’a tsaron farin kaya na DSS Yusuf Bichi.

Gwamnan Zamfaran, yace samun nasarar shirin afuwar zai kawo karshen matsalar hare-haren ‘yan bindigar a jihar da ma makwabtan ta, zalika zai karfafa tattalin arzikin wadanda suka ajiye makaman, ta hanyar neman halaliyarsu cikin ruwan sanyi, sai dai Bello Matawalle ya ce ba za bari ‘yan bindigar da suka tuba su sake koma cikin dazuka da sunan zama ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.