Isa ga babban shafi
Faransa-Sahel

Macron zai halarci taron kasashen Sahel a Mauritania

Shugaban Faransa Emmanuel Macron na shirin halartar taron shugabannin kasashen da ke cikin kungiyar G5 Sahel da zai gudana a Mauritania don tattauanwa kan batutuwan da suka shafi matsalolin tsaron da ya addabi yankin.

Shugaba Emmanuel Macron yayin wani taron G5 Sahel
Shugaba Emmanuel Macron yayin wani taron G5 Sahel Guillaume Horcajuelo/Pool via REUTERS
Talla

Taron na zuwa ne a daidai lokacin da ake cigaba da samun hare-hare ta’addanci dana tsageru da kuma kungiyoyin da ke dauke da makamai masu ikirarin jihadi a yankin, duk kuwa da kasancewar tarin Sojin Faransa da ke taimakawa a yaki da ta'addancin.

Cikin shugabannin da za su halarci taron na yau Talata, har da shugaban kasar Burkina Faso dana Mali kana na Nijar da Chadi da kuma shugaban Mauritania da ke matsayin mai masaukin baki.

Wannan dai ba shi ne karon farko da ake gudanar da makamancin taron ba, duk dai karkashin kokarin da ake na yaki hare-haren da yankin ke fuskanta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.