Isa ga babban shafi

Burundi: Yakin neman zabe ya kankama duk da barazanar coronavirus

An kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasar Burundi da zai gudana a watan gobe, duk da yadda annobar COVID-19 ke barazana ga shirin.

Wasu 'yan kasar Burundi, yayin gangamin siyasa.
Wasu 'yan kasar Burundi, yayin gangamin siyasa. The Independent Uganda
Talla

‘Yan takarar shugabancin kasar guda 7 ke shirin fafatawa a zaben da zai gudana ranar 20 ga watan Mayu, wanda ya kunshi zaben ‘yan majalisu da na kanana hukumomi.

Ya zuwa yanzu mutane 15 suka kamu da cutar coronavirus a Burundi, kuma mutum guda ya mutu daga cikinsu, yayinda 4 suka warke.

Yanzu haka dai Janar Evariste Ndeyishimiye jam’iyya mai mulki ta CNDD-FDD ta gabatar a matsayin wanda take fatan yam aye gurbin shugaba mai barin gado Pierre Nkrunziza, bayan shafe shekaru 15 yana mulki.

A shekarar 2015 kasar Burundi ta fada cikin tashin hankali mai nasaba da siyasa, bayanda shugaba Nkrunziza ya zarce karo na 3 kan mulkin kasar, abinda ya janyo mutuwar akalla mutane dubu 1 da 200, wasu kimanin dubu 400 kuma suka rasa muhallansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.