Isa ga babban shafi
Coronavirus

Dokar hana fita ta fara aiki a lardunan Accra da Kumasi na Ghana

Gwamnatin kasar Ghana ta haramta zirga-zirga a yankuna biyu mafi girma a kasar daga wannan litinin, domin dakile yaduwar cutar COVID-19 da ke ci gaba da halllaka jama’a a kasashen duniya.

Wani jami'in lafiya a birnin Accra yayin aikin tsaftace wuraren taruwar jama'a daga kwayar cutar coronavirus ko COVID-19. 23/3/2020.
Wani jami'in lafiya a birnin Accra yayin aikin tsaftace wuraren taruwar jama'a daga kwayar cutar coronavirus ko COVID-19. 23/3/2020. AFP / Nipah Dennis
Talla

Shugaban kasar Nana Akufo-Addo ya ce daukar matakin ya biyo bayan samun mutane 137 da suka kamu da cutar, yayin da tuni 4 suka rasa rayukansu.

Akufo-Addo ya bayyana yankunan da suka hada da Accra da kuma Kumasi, to sai dai ya ce matakin bai hana mutane fita domin sayen abinci da ruwan sha da magunguna ba, ko kuma amfani da ban dakin jama’a.

Shugaban ya ce dokar ta makwanni biyu ta haramta zirga zirgar jama’a daga gari zuwa gari a mota da jiragen sama, sai dai wadanda jami’an kula da lafiya ke aiki da su kawai.

Tuni Ghana ta bi sahun kasashen duniya wajen rufe makarantu da dakatar da ayyukan gwamnati da kuma hana taron jama’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.