Ecowas ta bukaci Guinea ta cire sunan wasu daga cikin rijistan zabe
Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta bukaci hukumomin kasar Guinea da su cire sunayen mutane miliyan da rabi daga cikin rajistar masu zabe saboda kasa tantance su da akayi kafin zaben da za’ayi a kasar.
Wallafawa ranar:
Wata tawagar kungiyar kwararru daga kungiyar ECOWAS da suka ziyarci Conakry domin taimakawa kasar shawo kan matsalolin zaben da take fuskanta ta dangane da zaben bayan korafi daga kasashen duniya ciki harda kungiyar Francophonie ta kasashe masu amfani da harshen Faransanci.
Hukumar zaben kasar tayi rajistar mutane sama da miliyan 7 da rabi ne, amma kuma sama da miliyan 2 da rabi sun kasa zuwa a tantance su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu