'Yan ta'adda sun kashe masu ungwanni 5 cikin kwanaki 3 a Nijar
Masu ungwanni biyar ne ake zargi ‘yan ta’adda sun kashe cikin kwanaki 3 a kudu maso yammacin Niger, kusa da iyaka da Mali.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wani dan majalisa daga jihar Tillaberi da bai so a bayyana sunansa bay a shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa daga ranar Alhamis zuwa Asabar aka kashe wadannan masu ungwannin.
An sace mutane 3 har ma da masu unguwanni da ba a tantance adadinsu ba a wasu kauyukan yankin.
A ranar 13 ga watan Nuwamba ma an kashe mai unguwar kauyen Bono, a Tillaberi, bayan an sace shi.
Tsakanin watan Afrilu da Yuli, an kashe akalla wasu masu ungwanni 3, da jami’en Tuareg 4 a harin da aka alakanta da kungiyar IS.
Kauyukan da suka sha wadannan hare – hare na wannan mako suna kusa da kauyen Tongo Tongo, kusa da iyaka da Mali, inda mayakan IS suka taba yin kwanton bauna har suka kashe dakarun Amurka 4 da na Nijar 4 a shekarar 2017.
Hare – haren ‘yan ta’adda sun tilasta wa dubban mutane barin kauyukan su zuwa kudancin kasar ta Nijar.
A karshen watan Oktoba, hukumar ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce mutane dubu 78 ne wannan al’amari ya daidaita a yammacin Tillaberi da Tahoua.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu