Isa ga babban shafi

Sojojin Masar sun hallaka 'yan ta'adda 83 a yankin Sinai

Dakarun Kasar Masar sun sanar da kashe ‘Yan tawaye 83 a Yankin Sinai dake fama da rikicin ‘yan ta’adda, Yankin da Kungiyar ISIS suka dade suna cin karen su babu babbaka.

Dakarun tsaron Masar a yankin Sinai na kasar
Dakarun tsaron Masar a yankin Sinai na kasar REUTERS/Mohamed Abd El Ghany
Talla

Jami’an tsaro Masar sun sanar da hallaka yan ta’adda 77, bayanda aka kama su da tarin makamai a arewaci da tsakiyar yankin Sinai.

Har ila yau, sanarwar da dakarun suka fitar na cewa a wani gagarumin farmaki na kasa domin kakkabe ‘yan ta’adda, wanda ya auku a tsakanin ranar 28 na watan Satumba zuwa ranar 4 ga watan Oktoban nan da muke ciki, Wasu tantiran yan tawaye 6 sun gamu da ajalinsu a yankin, yayin da wasu dakaru 3 suka jikkata.

Sanarwar ta ce a halin yanzu dai an kame mutane masu laifi 61, daga cikin su akwai wadanda aka shafe lokaci ana nema.

A farmakin da dakarun suka kai domin kakkabe ‘yan ta’addan, sun yi nasarar lalata sansanoni da kuma motocin mayakan da dama.

Kididdigar baya-bayan nan da jami’an tsaron suka fitar na nuna adadin ‘yan ta’addan da aka kashe a yankin Sinai ya haura 830.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.