Isa ga babban shafi
Gambia

Kotu na tuhumar tsohon ministan Jammeh bisa laifin kisa

Hukumomin kasar Gambia sun gurfanar da tsohon ministan gwamnatin Yahya Jammeh, Yankuba Touray a gaban kotu, saboda kin amsa tambayoyi a gaban Hukumar kasar ta Tantance Gaskiya da Sasanta Jama’a.

Yankuba Touray, tsohon ministan gwamnatin Yahya Jammeh.
Yankuba Touray, tsohon ministan gwamnatin Yahya Jammeh. Africa Feeds Media / Lamin Fadera
Talla

Touray wanda ke cikin tawagar tsohon shugaban da tayi juyin mulki a shekarar 1994, ya ce yana da kariyar da ta hana shi bada ba’asi a gaban hukumar.

Hukumar ta Tantance Gaskiya da Sasanta Jama’a na tuhumar tsohon ministan ne da hannu wajen kashe ministan kudin kasar ta Gambia a watan Yuni na shekarar 1995, da kuma sojoji a watan Nuwambar shekarar 1994.

Lauyan Touray Abdoulie Sissoho, ya bukaci bada belinsa da kuma cigaba da shari’ar a cikin wannan makon.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.