Isa ga babban shafi
Wasanni-Afrika

Kamaru ta lashe kofin Afrika na 'yan kasa da shekaru 17

Tawagar kungiyar kwallon kafar Kamaru ta ‘Young Indomitable Lions ta lashe kofin Afrika na ‘yan kasa da shekaru 17 bayan lallasa takwararta ta Guinea Syli Cadets da kwallaye 5 da 3 a bugun daga kai sai mai tsaron raga, yayin wasan da ya gudana jiya a birnin Der as Salam na Tanzania.

Tawagar kungiyar kwallon kafar Kamaru ta 'yan kasa da shekaru 17
Tawagar kungiyar kwallon kafar Kamaru ta 'yan kasa da shekaru 17 NAN
Talla

Kungiyoyin biyu dai sun yi canjaras ne a tsawon lokacin da aka dibar musu matakin da ya tilasta basu damar bugun daga kai sai mai tsaron raga, wanda kuma Kamarun ta yi nasara, a gasar wadda aka shafe mako 2 ana yi.

Kafin rashin nasara a hannun Kamaru, Guinea ta lallasa tawagar Najeriya ta Gne da kwallaye 10 da 9 shi ma dai a bugun daga kai sai mai tsaron ragar a shekaran jiya Asabar, yayinda itama Kamaru ta lallasa Angola ne a wasan ta na gab da na karshe.

Wannan dai ne karo na 2 da Kamaru ke samun nasarar dage kofin gasar cin kofin na Afrika amma fa na ‘yan kasa da shekaru 17.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.