Kamaru ta lashe kofin Afrika na 'yan kasa da shekaru 17
Tawagar kungiyar kwallon kafar Kamaru ta ‘Young Indomitable Lions ta lashe kofin Afrika na ‘yan kasa da shekaru 17 bayan lallasa takwararta ta Guinea Syli Cadets da kwallaye 5 da 3 a bugun daga kai sai mai tsaron raga, yayin wasan da ya gudana jiya a birnin Der as Salam na Tanzania.
Wallafawa ranar:
Kungiyoyin biyu dai sun yi canjaras ne a tsawon lokacin da aka dibar musu matakin da ya tilasta basu damar bugun daga kai sai mai tsaron raga, wanda kuma Kamarun ta yi nasara, a gasar wadda aka shafe mako 2 ana yi.
Kafin rashin nasara a hannun Kamaru, Guinea ta lallasa tawagar Najeriya ta Gne da kwallaye 10 da 9 shi ma dai a bugun daga kai sai mai tsaron ragar a shekaran jiya Asabar, yayinda itama Kamaru ta lallasa Angola ne a wasan ta na gab da na karshe.
Wannan dai ne karo na 2 da Kamaru ke samun nasarar dage kofin gasar cin kofin na Afrika amma fa na ‘yan kasa da shekaru 17.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu