Isa ga babban shafi
Senegal

Gwamnati ta yi ikirarin lashe zabe gabannin kidaya kuri'u

Fira Ministan Senegal Mahammed Boun Abdallah Dionne ya ce shugaba Macky Sall ya lashe zaben shugabancin kasar da aka gudanar jiya lahadi, a daidai lokacin da hukumar zabe ke aikin tattara sakamakon kuri’unda aka kada a ranar Lahadi.

Shugaban kasar Senegal Macky Sall.
Shugaban kasar Senegal Macky Sall. Photo: Seyllou/AFP
Talla

To sai dai biyu daga cikin ‘yan takara hudu da suka kara da shugaban a wannan zabe, wato tsohon Fira Minista Idrissa Sseck da kuma Ousmane Sanko sun ce sai an je zagaye na biyu kafin samun wanda zai lashe zaben.

Karo na farko kenan da zaben shugaban kasa zai gudana a Senegal bayan zaben raba gardama na shekarar 2016, wanda ya bada damar rage yawan shekarun da shugaba zai shafe bisa mulki daga shekaru 7 mai wa’adi daya, zuwa 5 bisa tsarin wa’adi biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.