Rundunar 'Yan sandan Najeriya ta yaye kurata dubu 6
Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Ibrahim Idris ya ce akalla kuratan ‘yan sanda dubu 6 aka yaye bayan sun samu horon watanni 7 a kwalejojin horar da ‘yan sanda na Maiduguri da Enugu da kuma Minna wadanda yanzu haka za a rarrabasu a sassan kasar don aikin tabbatar da tsaron al’umma.
Wallafawa ranar:
A cewar Ibrahim Idris yayin taron yaye kuratan da ya tura wakilci a kwalejojin 3, adadin wani bangare ne na ‘yan sanda dubu 10 da gwamnati mai ci ta sha alwashin samarwa da nufin karfafa tsaro a sassan Najeriyar.
Babban Sufetonn’yan sandan Najeriyar, ya ce ‘yan sandan wadanda dukkaninsu matasa ne masu jini a jika sun samu cikakken horon da za su bayar da gudunmawar da ta kamata, musamman a halin da kasar ke ciki na tabarbarewar al’amuran tsaro.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu