Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo-Zabe

Tarin jama'a sun jikkata a arangama tsakanin bangarorin adawar Congo

Wasu Majiyoyi a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo sun ce akalla mutum guda ya mutu, yayin da wasu sama da 80 suka samu raunuka, sakamakon arangamar da aka yi tsakanin magoya bayan jam’iyyun daban daban a zabe mai zuwa.

Rahotanni sun ce tsamin alaka na kara tsananta tsakanin magoya bayan na jam'iyyun adawa tun bayan karatowar zaben wanda ake sa ran ya sauya fasalin mulkin kasar.
Rahotanni sun ce tsamin alaka na kara tsananta tsakanin magoya bayan na jam'iyyun adawa tun bayan karatowar zaben wanda ake sa ran ya sauya fasalin mulkin kasar. © REUTERS
Talla

Rahotanni sun ce rikicin ya barke ne a Tshikapa da ke Yankin Kasai, lokacin da jiragen manyan 'yan siyasa biyu, Felix Tshesekedi da ministan ilimi Maker Mwangu suka sauka.

A baya-bayan nan ana yawan samun barkewar rikici musamman tsakanin bangarorin adawa a kasar ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo wanda a lokuta da dama kan kai ga asarar rayuka, yayinda a bangare guda hare-haren 'yan bindiga ke kara ta'azzara.

Kasar Congo na shirin gudanar da zaben shugaban kasa a karshen wannan mako, wanda ake saran ganin an zabi wanda zai maye gurbin shugaba Joseph Kabila da ya kwashe shekaru 17 a karagar mulki.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.