Isa ga babban shafi
Zimbabwe

Mutane 47 sun mutu a hatsarin mota a Zimbabwe

Akalla mutane 47 sun rasa rayukansu bayan wasu motocin safa biyu sun yi karo da juna a tsakanin birnin Harare da garin Rusape da ke yankin Kudu maso gabashin kasar Zimbabwe.

Mutane akalla 47 sun mutu a hatsarin mota a Zimbabwe
Mutane akalla 47 sun mutu a hatsarin mota a Zimbabwe pindula.co.zw
Talla

Jami’an ‘Yan sanda sun tabbatar da asarar rayukan da aka samu a hatsarin na ranar Laraba.

A wani sakon Twitter da ta wallafa a shafinta na Twitter, Jaridar Herald ta kasar ta ce, ba za ta iya wallafa hotunan hatsarin ba saboda muninsu.

Ana yawan samun hattsuran motoci a Zimbabwe saboda lalacewar hanyoyi bayan kwashe tsawon shekaru ba tare da kula da su ba.

Koda dai bayanai na cewa, a kwanan nan aka gyara hanyar da hatsarin baya-bayan ya auku.

A shekarar bara, an samu mutane 43 da suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota a yankin arewacin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.