Najeriya
An kashe mataimakin jakadan Najeriya a Sudan
Jami’an tsaron kasar Sudan sun tabbatar da kisan jami’in Diflomasiyyar Najeriya da ke kasar wanda aka yiwa kisan gilla ta hanyar daba masa wuka a gidansa da ke birnin Khartoum a yau Alhamis.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumomi a Sudan din sun ce kawo yanzu ba a kammala bincike don gano wadanda ke da hannu a kisan jami’in ba.
Haka zalika Ofishin jakadancin Najeriya a birnin na Khartoum bai ce uffan kan batun ba.
Duk da cewa dai Sudan din ta yi fama da karancin tsaro a baya, amma kisan jami'in Diflomasiyya har gida a birnin Khartoum sabon abu ne.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu