Isa ga babban shafi
Najeriya

An kashe mataimakin jakadan Najeriya a Sudan

Jami’an tsaron kasar Sudan sun tabbatar da kisan jami’in Diflomasiyyar Najeriya da ke kasar wanda aka yiwa kisan gilla ta hanyar daba masa wuka a gidansa da ke birnin Khartoum a yau Alhamis.

Shugaban kasar Sudan Omar Hassan al Bashir a fadar gwamnatin Najeriya.
Shugaban kasar Sudan Omar Hassan al Bashir a fadar gwamnatin Najeriya. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Hukumomi a Sudan din sun ce kawo yanzu ba a kammala bincike don gano wadanda ke da hannu a kisan jami’in ba.

Haka zalika Ofishin jakadancin Najeriya a birnin na Khartoum bai ce uffan kan batun ba.

Duk da cewa dai Sudan din ta yi fama da karancin tsaro a baya, amma kisan jami'in Diflomasiyya har gida a birnin Khartoum sabon abu ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.