Zimbabwe
Ana tuhumar Grace Mugabe kan safarar hauren-giwa
'Yan Sanda a Zimbabwe na gudanar da bincike kan matar tsohon shugaban kasar, Robert Mugabe kan zargin da ake ma ta na safarar hauren giwa zuwa kasashen waje.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni sun ce, Jami’an Kula da Gandun Dajin kasar sun mika wa 'yan sandan tarin bayanai dangane da yadda Grace Mugabe ta rika safarar hauren zuwa China da Daular Larabawa da kuma Amurka.
Kakakin 'yan sanda, Charity Charamba ta tabbatar da samun bayanan daga jami’an gandun dajin.
Christopher Mutsvangwa, jami’i a fadar shugaban kasar ya ce, wani jami’i ne ya tsegunta wa gwamnati labarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu