Zanga-zangar nuna bacin rai a kasar Morocco
Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zanga a birnin Jerada da ke arewacin Morocco don nuna fushi dangane da mutuwar mutane biyu a wata mahakar ma’adinai.
Wallafawa ranar:
A yau litinin da dama daga cikin masu zanga-zangar ne suka sake fitowa don gani hukumomin sun dau matakan da suka dace don kawo karshen wannan matsalla a yankin na Jerada.
Masu zanga-zangar na zargin mahukunta da nuna sakaci ta hanyar kin killace wannan tsohuwar mahakar ma’adinai da aka daina aiki a cikinta tsawon shekaru.
Kasar Morocco na daya daga cikin kasashen Afrika dake hako gawayi da kuma ke sayar da shi .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu