Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa ta nemi Majalisar Dinkin Duniya ta dau mataki kan Libya

KASAR Faransa ta ce ya zama wajibi Majalisar Dinkin Duniya ta dauki mataki mai tsauri kan kasar Libya domin kawo karshen cinikin bayin da ake samu a kasar. Tun bayan gano badakalar cinikin bayin a Libyan Faransa ke ci gaba da nuna rashin jin dadi tare da yin Tir da batun.

Faransa ta ce dole ne a dauki tsauraran matakai kan Libya ba wai batun ya tsaya a barazanar fatar baki kadai ba.
Faransa ta ce dole ne a dauki tsauraran matakai kan Libya ba wai batun ya tsaya a barazanar fatar baki kadai ba. REUTERS/Ludovic Marin/Pool
Talla

Jakadan Faransa a Majalisar Francois Delattre ya bayyana haka kafin taron da kasar sa ta kira na kwamitin Sulhu yau talata domin tattauna matsalar.

Delattre yace ya zama dole Majalisar ta zarce Magana ta fatar baki wajen daukar mataki a aikace kan wannan mummunar matsala da aka samu.

Jakadan ya shaidawa manema labarai a birnin New York cewar bai kauda shakkun sanyawa kasar takunkumi ba saboda girmar matsalar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.