Isa ga babban shafi
Kamaru

Gwamnatin Kamaru ta fara tattaunawa da shugabannin yankin Bamenda

Fira Ministan kasar Kamaru, Philemon Yang, ya fara wata ziyarar tuntubar juna a yankin Bamenda, dake arewa maso gabashjin kasar, a kokarin da gwamnatinsu ke yi na na tattaunawa da mutanen yankin, dake amfani da turancin inglishi a yankin, wanda a baya yayi fama da rikice rikicen siyasa da na zamantakewa.

Wani sashi na yankin Bamenda mai amfani da turancin Ingilishi a kasar Kamaru, a lokacin gudanar da zanga zangar adawa da gwamnati, bisa zargin nuna musu banbanci. Ranar 8 ga Disamba, 2016.
Wani sashi na yankin Bamenda mai amfani da turancin Ingilishi a kasar Kamaru, a lokacin gudanar da zanga zangar adawa da gwamnati, bisa zargin nuna musu banbanci. Ranar 8 ga Disamba, 2016. REUTERS/Stringer
Talla

Mista Yang ya gana shuwagabannin kungiyoyin sufuri, malaman makaranta, ‘yan kasuwa, shugabanin kamfanoni, da kuma bankuna a yankin na Bamenda.

Wadanda suka halarci tattaunawar ta jiya Litanin sun gabatarwa Fira Ministan shawarwari kan yadda za’a magance matsalolin yankin, sai dai kuma babu cikakken bayani kan abinda shawarwarin suka kunsa.

Yau Talata ma, gwamnatin kasar ta Kamaru za ta ci gaba da tattaunawar da jagororin yankin na arewa maso yammaci

A baya dai yankin na masu amfani da turancin Ingilishi ya shafe watanni ana zaman dar dar cikinsa sakamakon zazzafar adawa da mutanen yankin ke yi da gwamnatin Paul Biya wadda suka zarga da nuna musu banbanci wajen fifita yankunan da ke amfanin da Faransanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.